Nigeria TV Info â Rahoton Labarai
Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da dawo da Makarantar Koyar da Rundunar Sojin Musamman daga Buni Yadi da ke Jihar Yobe zuwa Karamar Hukumar Doma a Jihar Nasarawa.
Babban Hafsan Sojin Kasar (COAS), Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ne ya bayyana hakan yayin bikin sanya tubalin ginin wasu sabbin ayyuka a hedikwatar Rundunar Special Forces ta 4 da ke Doma.
A cewar Oluyede, wannan mataki na daga cikin shirye-shiryen inganta dabarun aiki da kuma samar da sauÆi wajen samun kayayyakin aiki da na horo domin magance Æalubalen tsaro da ke Æaruwa a faÉin Æasar.
Ya Æara da cewa kafa makarantar horaswar a Jihar Nasarawa zai kuma Æara Æarfafa tsaro a yankin Arewa Ta Tsakiya tare da bada gudummawa wajen ci gaba da ÆoÆarin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Æasar.
Babban Hafsan Sojin ya kuma tabbatar da ci gaba da jajircewar rundunar sojin wajen kare rayuka da dukiyoyin jamaâa, inda ya jaddada cewa wannan sauye-sauye na daga cikin muhimman matakan da za su Æarfafa tsarin tsaro na Æasar baki Éaya.
Oluyede ya yi amfani da wannan dama wajen yabawa jamiâai da sojojin rundunar Special Forces bisa ÆoÆari da sadaukarwar da suke nunawa wajen yaÆi da taâaddanci, âyan bindiga da sauran aikace-aikacen laifi a faÉin Æasar.
Sharhi