Amurka da Iran Sun Gagara Cimma Yarjejeniya Bayan Tattaunawa a Islamabad
Amurka da Iran sun kasa cimma wata muhimmiyar yarjejeniya bayan tattaunawar zaman lafiya da aka gudanar a Islamabad, Pakistan, inda Amurka ta ce ta gabatar da abin da ta kira “tayin ta na ƙarshe kuma mafi kyau.”
Tattaunawar ta ƙare ba tare da cimma matsaya ba bayan kwanaki na shawarwari domin rage rikicin da ya dade tsakanin ƙasashen biyu.
Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance, ya ce tawagar Iran ta ƙi amincewa da sharuɗɗan da Amurka ta gabatar, yana mai cewa wannan ita ce dama ta ƙarshe a wannan tsarin tattaunawa.
Iran ta mayar da martani inda ma’aikatar harkokin wajen ta ta bukaci Amurka da ta guji “tsauraran buƙatu,” tana mai cewa tattaunawar ta gudana ne cikin yanayi na rashin yarda da juna.
Sharhi